
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Ogun State ta kama wani malamin makaranta mai zaman kansa mai shekaru 30, Nathaniel Baiyegun, bisa zargin kashe wata yarinya mai shekaru 16 mai suna Florence, wacce tsohuwar ɗalibarsa ce kuma tana shirin sake rubuta jarabawar WASSCE.
Rahotanni sun bayyana cewa wanda ake zargin ya yaudari yarinyar da sunan zuwa koyon darussa na musamman, kafin daga bisani ya kai ta wani gini da ba a kammala ba inda ya ɓoye ta.
Bincike ya nuna cewa ya ba yarinyar ƙwayoyin barci da yawa bayan ta koka da rashin samun barci, lamarin da ya jawo ta shiga mawuyacin hali.
A bayanin da ya bai wa ’yan sanda, wanda ake zargin ya ce shi da Florence sun shirya wata dabarar bogin garkuwa da ita domin karɓar kuɗi daga iyayenta. Ya bayyana cewa ya yi amfani da wayarta wajen neman kuɗin fansa daga mahaifinta.
Sai dai ya ce bayan ya dawo daga wani taro, ya tarar da yarinyar cikin mawuyacin hali. Maimakon neman taimakon gaggawa, ya ɗauke ta zuwa wani kogi da ke yankin Ogijo inda ya jefar da gawarta bayan ya yi zaton ta mutu.
Rahotanni sun ƙara da cewa duk da mutuwar yarinyar, wanda ake zargin ya ci gaba da yaudarar iyayenta, inda ya karɓi Naira 500,000 a matsayin kuɗin fansa tare da yi musu alƙawarin cewa za a sako ta.
Daga baya, ya amsa cewa ya kashe mafi yawan kuɗin wajen yin caca ta yanar gizo.
Rundunar ’yan sandan jihar ta tabbatar da kama wanda ake zargin, tare da bayyana cewa ana ci gaba da gudanar da bincike domin gano cikakkun bayanai kan lamarin kafin gurfanar da shi a gaban kotu.
