
Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa fannin ma’adanai na Najeriya ya jawo jarin da ya kai dala biliyan 3 a cikin shekaru uku da suka gabata, inda ta bayyana shigar da kudin a matsayin daya daga cikin manyan nasarorin da aka samu a tarihin masana’antar
Gwamnatin ta ce wannan cigaban ya nuna karuwar kwarin gwiwar masu zuba jari da kuma muhimmancin gyare-gyaren da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ke gabatar wa a fannin, lamarin da ya nuna karin kwarin gwiwar samun cigaba ga fannin a cikin shekaru masu zuwa.
An bayyana hakan ne a wani taron manema labarai da aka yi kafin taron zuba jari na Albarkatun Kasa da Makamashi na Afirka karo na 5 da aka shirya gudanarwa daga ranar 23 ga Yuni zuwa 25 ga Yunin shekarar nan ta 2026, a Cibiyar Taro ta Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja.
Kano first

Ministan Raya Ma’adanai Dakta Dele Alake, wanda Babban Jami’in Gudanarwa na Kamfanin Ma’adanai na Najeriya, Martins Imonitie, ya wakilta ya ce masana’antar ma’adinai ta fara jawo hankalin masu zuba jari.
A cewarsa, jawo hankalin masu zuba jarin da ya kai dala biliyan 3 cikin shekaru uku abu ne da ba a taba ganin irinsa ba.
