Hukumar Zabe ta Kasa INEC ta nemi mutanen da suka yi rijistar katin zabe a Jihar Kano da su je su duba sunayensu, yayin da hukumar za ta wallafa jerin sunayen daga ranar Laraba 29 ga Afrilu zuwa ranar Talata 5 ga Mayun 2026.
Brown pigeon ta rawaito cewa, wannan na cikin sanarwar da ofishin hukumar zaben reshen Jihar Kano ya fitar a ranar Litinin 27 ga Afrilu 2026.
Sanarwar ta bayyana cewa hukumar za ta kafe sunayen a ofisoshinta da ke kananan hukumomi 44 na jihar.
Hukumar ta bukaci wadanda suka yi rijistar su duba sunayensu domin gano kura-kurai domin a gyara, inda ta ce hakan zai taimaka wajen sake tantance bayanai da kuma cire sunayen mutanen da suka mutu, da wadanda ba yan kasa ba, da kuma wadanda shekarunsu ba su kai ba daga jerin rijistar zaben.
Hukumar ta kuma bukaci jama’a su gabatar mata da rahoton duk wani kuskure da suka gano a bayanan rijistarsu domin a dauki matakin gyara akan lokaci.

