
Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano (HMB) ta bayyana cewa ba za ta lamunci rashin zuwa aiki, sakaci ko kuma karya jadawalin aiki (Shift da Call Duty) da aka amince da shi a dukkan asibitocin mataki na biyu da ke fadin jihar.
Sakataren Zartarwa na Hukumar, Dakta Mansur Mudi Nagoda, ne ya bayyana hakan yayin wasu ziyarce-ziyarcen bazata da ya kai manyan asibitocin jihar domin tantance jajircewar ma’aikata wajen aiki, ingancin ayyukan kiwon lafiya da kuma yadda cibiyoyin ke gudanar da ayyukansu.
Dakta Nagoda ya nuna matukar damuwarsa kan yadda wasu ma’aikatan lafiya ke barin wuraren aikinsu duk da cewa suna cikin jadawalin masu aiki ko masu jiran kiran gaggawa, inda ya bayyana hakan a matsayin rashin kwarewa, rashin da’a da kuma barazana ga rayukan marasa lafiya.
Ya ce, “Ba daidai ba ne ma’aikatan lafiya da aka dora wa alhakin ceton rayuka su rika barin wuraren aikinsu, Irin wannan hali na jefa marasa lafiya cikin hadari tare da rage amincewar jama’a da tsarin kiwon lafiyarmu.”
Kano first

Sakataren Zartarwan ya gargadi ma’aikatan cewa daga yanzu Hukumar za ta dauki tsauraran matakan ladabtarwa kan duk wanda aka samu da laifin karya jadawalin aiki. Ya ce duk wanda aka samu da laifi zai rasa alawus-alawus din da ya shafi aikin kira ko aikin lokaci, baya ga sauran hukuncin gudanarwa da dokokin aikin gwamnati suka tanada.
Dangane da bunkasa karin ma’aikata, Dakta Nagoda ya bayyana cewa Gwamnatin Jihar Kano na ci gaba da kokarin kammala daukar karin kwararrun ma’aikatan lafiya domin cike gibin da ake da shi a asibitocin jihar. Sai dai ya bukaci shugabannin asibitoci da su yi amfani da ma’aikatan da ake da su cikin hikima da kwarewa wajen ingancin su har zuwa lokacin da za’a kammala daukar sabbin ma’aikatan.
Ya kuma bayyana cewa Hukumar ta kara karfafa tsarin sa ido da tantance ayyuka domin tallafawa kudirin gwamnati na inganta ayyukan kiwon lafiya da tabbatar da cewa al’umma suna samun kulawar lafiya mai inganci cikin sauki da kuma kan lokaci.
A wani mataki na tabbatar da da’a da rikon amana, an kuma bai wa wasu ma’aikatan da aka samu da laifuka yayin ziyarar takardun neman bayani wato (Query) nan take.
A matsayin wani bangare na inganta rikon amana da gudanar da aiki yadda ya kamata, Dakta Nagoda ya umarci dukkan shugabannin asibitoci da su tabbatar da manna sabbin jadawalin ayyukan yau da kullum a dukkan sassa da bangarorin asibitocin. Haka kuma ya jaddada muhimmancin tsafta da kula da muhalli a cibiyoyin lafiya domin samar da yanayi mai kyau ga marasa lafiya.
Tawagar binciken karkashin jagorancin Dakta Mansur Mudi Nagoda tare da daraktocin Hukumar ta ziyarci manyan cibiyoyin lafiya da suka hada da Asibitin Kwararru na Murtala Muhammad, Asibitin Sheikh Jidda, Asibitin Cututtuka Masu Yaduwa, Asibitin Waziri Gidado, Cibiyar Kula da Matsalolin mafitsara ta Abubakar Imam da Asibitin Mallam Ja’afar da sauransu.
Gwamnatin Jihar Kano ta sake jaddada kudirinta na gina tsarin kiwon lafiya mai inganci, mai saurin amsa bukatun jama’a kuma mai mayar da hankali kan marasa lafiya, inda kwarewa, sadaukarwa da rikon amana za su kasance ginshikan gudanar da ayyukan lafiya.
ZS/ RAM.