
Daga Mutawakkilu Ibrahim Idris
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sake nuna ƙwarewa da jajircewa a harkokin gudanar da aikin Hajji, inda ta bayyana cewa ta kammala dukkan shirye-shiryen jigilar maniyyata zuwa Ƙasa Mai Tsarki domin aikin Hajjin shekarar 2026.
Shugaban Hukumar, Alhaji Abubakar Ibrahim Matawalle, ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai jim kaɗan bayan ƙaddamar da shirin allurar rigakafi ga maniyyata a Asibitin Sansanin Alhazai na Jihar Kano.
Ya ce hukumar ta samu gagarumar nasara wajen kammala bayar da biza kashi 100 ga dukkan maniyyatan da suka nemi aikin Hajjin bana, yana mai bayyana hakan a matsayin wata alama ta ƙudurin Gwamnatin Jihar Kano na samar da ingantattun ayyuka da kula da jin daɗin al’umma.
Matawalle ya ƙara da cewa an tanadi dukkan muhimman abubuwan da suka haɗa da sufuri, takardu, da kuma matakan kiwon lafiya domin tabbatar da cewa jigilar maniyyatan za ta gudana cikin tsari, tsaro da nasara ba tare da tangarda ba.
Ya kuma jaddada cewa hukumar za ta ci gaba da mayar da hankali wajen tabbatar da cewa maniyyata daga jihar sun gudanar da aikin Hajji cikin sauƙi da natsuwa.
A nata jawabin, Daraktar Hukumar Kula da Lafiya a Tashoshin Shiga da Fita ta Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya, Dr. Bilkisu Jibiril Idris, ta yaba wa Gwamnatin Jihar Kano da kuma shugabancin Hukumar Jin Daɗin Alhazai bisa kyakkyawan tsari da bin ƙa’idojin lafiya.
Ta bayyana shirin allurar rigakafin a matsayin abin koyi, tana mai cewa Jihar Kano ta nuna fifiko a kan sauran jihohin da ta ziyarta ta fuskar tsari, haɗin kai da kuma ƙwarewa wajen gudanar da rigakafin maniyyata.
