
Daga Mutawakkilu Ibrahim Idris
An gudanar da wani shirin wayar da kai ga matasa maza da mata kan muhimmancin mallakar katin zaɓe a harabar Kwalejin Ilimi ta Tarayya (FCE) da ke Bichi a Jihar Kano.
Shirin ya gudana ne ƙarƙashin jagorancin Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kano, comared Ibrahim Abdullahi Waiya, a wani ɓangare na ƙoƙarin gwamnatin jihar na ƙara wayar da kan matasa game da muhimmancin shiga harkokin dimokuraɗiyya da kuma amfani da haƙƙinsu na zaɓe.
A jawaban da aka gabatar yayin taron, an jaddada cewa katin zaɓe wata muhimmiyar hanya ce da ke bai wa ‘yan ƙasa damar zaɓar shugabannin da suke so cikin tsarin dimokuraɗiyya. An kuma ƙarfafa wa ɗalibai da sauran matasa gwiwa da su tabbatar sun yi rajista tare da mallakar katin zaɓe domin su taka muhimmiyar rawa wajen gina makomar ƙasa.
Kano first

Masu jawabin sun bayyana cewa matasa su ne kaso mafi yawa na al’umma, don haka ya zama wajibi su kasance cikin sahun gaba wajen shiga harkokin zaɓe da bayar da gudunmawa ga ci gaban al’umma ta hanyar zaɓen shugabanni nagari.
Taron ya kuma bai wa mahalarta damar yin tambayoyi tare da samun ƙarin haske kan hanyoyin yin rajistar katin zaɓe da muhimmancin amfani da shi a lokacin zaɓe.
Wasu daga cikin ɗaliban da suka halarci shirin sun yaba da wannan yunƙuri, suna mai cewa ya ƙara musu fahimta kan rawar da katin zaɓe ke takawa wajen tabbatar da kyakkyawan shugabanci da ci gaban dimokuraɗiyya.
Shirin na daga cikin matakan da gwamnatin Jihar Kano ke ɗauka na wayar da kan al’umma, musamman matasa, kan muhimmancin shiga harkokin siyasa da dimokuraɗiyya cikin lumana da bin doka.
