
Gwamnatin Jihar Kano ta kaddamar da kwamiti na musamman domin tsara gudanar da yadda bikin cika shekaru uku na mulkin Gwamna Abba Kabir Yusuf.
An kaddamar da kwamitin ne a madadin Gwamnan Jihar Kano ta hannun Sakataren Gwamnatin Jihar Alhaji Umar Faruk Ibrahim, wanda ya bukaci mambobin kwamitin da su tsara gagarumin biki mai cike da armashi wanda zai bayyana nasarorin da gwamnatin mai ci ta samu cikin shekaru uku.
Da yake jawabi yayin bikin kaddamar da kwamitin da aka gudanar a dakin taro na Ofishin Majalisar Zartarwa (Cabinet Office Conference Hall) da ke Kano, Alh Umar Faruq ya ce bikin zai zama wata dama ta bayyana irin ci gaban da gwamnatin ta samu a fannoni daban-daban da suka hada da gine-ginen more rayuwa, ilimi, lafiya, noma, muhalli, ci gaban karkara da kuma kyakkyawan shugabanci.
A cewarsa, ana sa ran bikin zai samu halartar manyan baki da fitattun mutane daga ciki da wajen Jihar Kano, tare da bai wa gwamnatin Jihar Kano damar nuna nasarorinta ga Al’ummar Jihar .
Alhaji Umar Faruk Ibrahim, wanda shi ne Shugaban Kwamitin, ya jaddada muhimmancin bayanan ayyukan da za a gudanar. Ya bayyana cewa za a wallafa wani littafin mai dauke da cikakkun bayanai kan manyan nasarorin da gwamnatin ta cimma domin tarihin ga masu tasowa a nan gaba.
Kwamitin ya kunshi manyan jami’an gwamnati da suka hada da kwamishinoni, masu ba da shawara na musamman, daraktoci da sauran manyan ma’aikatan gwamnati.
Daga cikin mambobin kwamitin akwai
Injiniya Marwan Ahmad, Kwamishinan Ayyuka (Works)
Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida
Dakta Abubakar Labaran Yusuf, Kwamishinan Lafiya
Dakta Dahir Muhammad Hashim, Kwamishinan Muhalli da Sauyin Yanayi
Dakta Danjuma Mahmoud, Kwamishinan Noma da Albarkatun Kasa
Dakta Gwani Ali Haruna Abubakar Makoda, Kwamishinan Ilimi
Hon. Abduljabbar Umar Garko, Kwamishinan Filaye da Tsare-tsaren Birane
Hon. Abdulkadir Abdussalam, Kwamishinan Raya Karkara da Al’umma
Hon. Adda’u Lawan Kutama, Mai Ba da Shawara na Musamman, Ofishin Majalisar Zartarwa
Alhaji Sunusi Bature Dawakin Tofa, Darakta Janar na Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a
Hon. Abdullahi Ibrahim Rogo, Darakta Janar na Harkokin Tsare-tsare da Ladabi (Protocol)
Hajiya Nana Asma’u Jibrin, Darakta Janar na Bincike da Adana Bayanai
Hon. Baffa Babba Dan Agundi, Darakta Janar na Cibiyar Ƙara Ƙwazo ta Ƙasa
Hon. Musa Illiyasu Kwankwaso
Haka kuma, Alhaji Umar Muhammad Jalo, Babban Sakatare na Sashen Bincike, Tantancewa da Harkokin Siyasa (REPA), zai kasance Sakataren Kwamitin.
