
Gwamnatin Jihar Kano ta sake nanata aniyarta na kammala manyan ayyukan more rayuwa da ake gudanarwa a fadin jihar, inda ta bayyana cewa za a kammala gadar sama ta Dan’Agundi da ke kan titin BUK kafin karshen wannan wata.
Haka zalika, gwamnati ta bayar da tabbacin kammala gadar sama ta Tal’udu, tana mai cewa ayyukan duka biyun na tafiya yadda ya kamata kuma za a mika su kamar yadda aka tsara.
Kwamishinan Ayyuka, Injiniya Marwan Ahmed, ne ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai bayan rangadin duba ayyuka da wata tawagar Gwamnatin Tarayya karkashin jagorancin Mai Bai wa Shugaban Kasa Shawara kan Harkokin Yada Labarai da Hulda da Jama’a, Sunday Dare, ta kai a jihar.
A yayin ziyarar, Injiniya Marwan Ahmed tare da Kwamishinan Yada Labarai da Harkokin Cikin Gida, Kwamared Abdullahi Waiya, da Kwamishinan Muhalli, Dakta Dahiru Hashim, sun duba yadda ayyuka daban-daban ke gudana, ciki har da aikin titin Wuju Wuju.
Ya bayyana cewa aikin titin Wuju Wuju mai tsawon kilomita bakwai ya samu gagarumin ci gaba, inda aka riga aka kammala kilomita guda.
Kwamishinan ya kuma kara da cewa gwamnatin jihar ta nemi tallafi daga Gwamnatin Tarayya domin tabbatar da kammala sauran sassan aikin cikin lokaci. A martaninta, Gwamnatin Tarayya ta ware sama da naira biliyan 40 daga Asusun Ecological domin tallafa wa aikin.
A cikin rangadin, tawagar ta kuma ziyarci sabbin cibiyoyin kula da cututtukan zuciya da aka gina tare da duba ayyukan gyare-gyare da ake yi a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano. Haka kuma, sun duba aikin girka karamin tsarin samar da wutar lantarki ta hasken rana (solar mini-grid) a asibitin, domin inganta samar da wuta da kyautata ayyukan jinya.
Bugu da kari, tawagar ta kai ziyara zuwa manyan asibitocin da ake yi wa gyaran fuska, ciki har da Asibitin Koyarwa na Muhammad Abdullahi Wase da Asibitin Yara na Hasiya Bayero, a wani bangare na kokarin gwamnatin jihar na bunkasa harkokin kiwon lafiya.
An bayyana wadannan shirye-shirye a matsayin wadanda suka yi daidai da manufar “Renewed Hope” ta gwamnatin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, wadda ta mayar da hankali kan bunkasa ababen more rayuwa, inganta harkokin kiwon lafiya da samar da makamashi mai dorewa a fadin kasar.
Ziyarar na daga cikin kokarin da ake yi na sa ido domin tabbatar da ingantaccen aiwatar da ayyuka da kuma kammala su a kan lokaci a fadin jihar.
