
Daga Mohammed Babagana Abubakar
A kowace al’umma mai tsarin dimokuradiyya, gasa ta siyasa da muhawarar jama’a suna daga cikin ginshiƙan shugabanci nagari. Jihar Kano, wadda ta yi fice wajen wayewar siyasa da ƙwarewar al’amuran jama’a, ta kasance cibiyar tattaunawa da muhawara kan harkokin mulki. Sai dai kuma akwai lokutan da ya zama wajibi a fifita muradun al’umma gaba ɗaya fiye da muradun wasu tsirarun mutane ko ƙididdigar siyasa. Wannan ne irin lokacin da Kano ke ciki a yau.
A ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf, jihar Kano ta shiga wani sabon zamani na mayar da hankali kan kyakkyawan shugabanci, gyaran cibiyoyi, bunƙasa ababen more rayuwa, da inganta walwalar jama’a. Tun bayan hawansa mulki, gwamnatin ta himmatu wajen dawo da amincewar jama’a ga gwamnati tare da tabbatar da cewa cigaba ya isa ga al’ummomin da ke cikin ƙananan hukumomi 44 na jihar. A yau, ana ganin sakamakon waɗannan ƙoƙari a fannoni daban daban kamar ilimi, lafiya, tsaro da kuma ƙarfafa matasa.
Yayin da ake ci gaba da tattaunawa kan yiwuwar yin garambawul a majalisar zartarwa ta jihar, abu ne na al’ada a tsarin mulki a ga masu ruwa da tsaki suna nuna sha’awa da fata. Garambawul a gwamnati wani ɓangare ne na shugabanci wanda ake amfani da shi domin ƙara inganci da bunƙasa ayyukan gwamnati. Amma irin waɗannan matakai ya kamata su kasance bisa kimanta aiki da nasarorin da aka samu, ba wai saboda matsin lamba na siyasa ko neman biyan bukatun wasu mutane ba.
Abin takaici, wasu alamu sun nuna cewa akwai wasu ‘yan siyasa da ke ƙoƙarin amfani da wannan yanayi domin ciyar da muradunsu na kashin kai gaba. Rahotannin yakin neman mukamai a bayan fage, amfani da wakilai wajen yada manufofi, da kuma wasu dabaru na matsin lamba sun fara karkatar da hankali daga muhimman ayyukan gwamnati. Duk da cewa kowane ɗan ƙasa na da damar neman mukamin gwamnati, bai kamata a mayar da mulki wata fafatawa ta neman kujeru ba har ta kai ga kawo cikas ga cigaban da ake samu.

Ɗaya daga cikin ma’aikatun da suka fi daukar hankalin jama’a a wannan lokaci ita ce Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida, ƙarƙashin jagorancin Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya. Tun bayan naɗinsa, an shaida gagarumin sauyi a yadda ma’aikatar ke gudanar da harkokin sadarwa da hulɗa da jama’a. Bisa gogewarsa a harkokin ƙungiyoyin fararen hula da aiki a matakin al’umma, Waiya ya taimaka wajen mayar da ma’aikatar wata gada tsakanin gwamnati da talakawa, maimakon ta kasance kawai cibiyar fitar da sanarwar gwamnati.
Baya ga harkokin sadarwa, ma’aikatar ta taka muhimmiyar rawa wajen tallafawa shirye shiryen da suka shafi zaman lafiya da tsaron al’umma. Shirye shirye irin su Safe Corridor Initiative sun nuna ƙudirin gwamnati na magance tushen matsalolin tsaro ta hanyoyin zaman lafiya, wayar da kan matasa da sake gyara rayuwar waɗanda ke cikin haɗari. Haka kuma, ƙarfafa tsarin tsaro na al’umma da haɗa matasa cikin ayyukan tsaro ya ƙara taimakawa wajen tabbatar da zaman lafiya a sassa daban daban na jihar.
Wadannan nasarori ba sa nufin cewa babu wanda za a iya tantance aikinsa ko sauya shi. A tsarin dimokuradiyya, alhaki da yin aiki yadda ya kamata suna da muhimmanci. Amma abin da ya kamata ya kasance ma’aunin hukunci shi ne nagartar aiki da sakamakon da aka samu. Sauya shugabanci mai inganci domin kawai gamsar da wasu bukatun siyasa ko samar wa wasu dandali na cimma burinsu na gaba na iya janyo koma baya ga ayyukan da ake gudanarwa da kuma ci gaban cibiyoyi.
Ƙarfin kowace gwamnati ba ya ta’allaka ne kawai ga hangen nesan shugabanta ba, har ma da ƙwarewa, jajircewa da amincin mutanen da aka ɗora wa alhakin aiwatar da wannan hangen nesa. Kyakkyawan shugabanci na buƙatar daidaito, ci gaba da tsare tsare, da kuma kiyaye ƙwarewar da aka tara tsawon lokaci. Duk wani sauyi da ya samo asali daga son zuciya ko matsin lambar siyasa maimakon tantance aiki na iya raunana cibiyoyin da ake buƙata domin tabbatar da ci gaba mai ɗorewa.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nuna a lokuta da dama cewa yana fifita muradun jama’a sama da anfani na siyasa. Mayar da hankalin gwamnatinsa kan ilimi, lafiya, tsaro da walwalar al’umma ya nuna cewa manufarsa ita ce samar da sakamako mai ɗorewa ga al’umma. Kare wannan mayar da hankali zai kasance muhimmi yayin da gwamnati ke shirin shiga sabon mataki na aiwatar da manufofinta.
A wannan muhimmiyar gaɓa, ya zama wajibi ga masu ruwa da tsaki, magoya baya da sauran al’umma su guji duk wani yunƙuri na karkatar da hankali daga harkokin cigaba. Neman mukami hakki ne na kowane ɗan ƙasa, amma bai kamata ya zama sama da muradun jama’a ba. Ya kamata tattaunawa ta mayar da hankali kan yadda za a ƙara bunƙasa jihar, ƙarfafa cibiyoyi, samar da damammaki ga matasa, da kuma inganta rayuwar al’umma baki ɗaya.
A ƙarshe, nasarar kowace gwamnati tana dogara ne da yadda take iya ci gaba da aiwatar da manufofinta ba tare da shagaltuwa da hayaniyar siyasa ba. Jihar Kano ba za ta iya ɗaukar nauyin rashin kwanciyar hankali ko wasu dabarun siyasa da za su iya kawo cikas ga cigaban da ake samu ba. Abin da ya kamata ya kasance a gaba shi ne kare manufa, tabbatar da dorewar nasarorin da aka samu, da kuma ci gaba da aiwatar da manufofin da za su amfani al’ummar Kano baki ɗaya.
