
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ba da umarnin gudanar da cikakken bincike domin gano musabbabin rasuwar Maimuna Sani Nihal, daliba a Makarantar St. Louis da ke jihar.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Babbar Mai Taimakawa Gwamnan Jihar Kano kan Ilimin ‘Ya’ya Mata, Hafsat Adhama, ta fitar.
Sanarwar ta bayyana cewa Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano ya fara aiwatar da umarnin gwamnan, domin gudanar da bincike mai zurfi kan lamarin tare da tabbatar da cewa an yi adalci.

Ta ce Hafsat Adhama za ta ci gaba da sa ido kan yadda ake gudanar da binciken, tare da gabatar wa gwamna rahoto kan sakamakon da za a samu.
Gwamnatin Jihar Kano ta kuma jajanta wa iyalan marigayiyar Maimuna Nihal bisa wannan babban rashi, tare da tabbatar da cewa ba za ta lamunci duk wani abu da ya saba wa doka ko adalci ba idan bincike ya tabbatar da hakan.
Hakazalika, gwamnatin ta bukaci al’umma da su kwantar da hankalinsu, su kuma guji yada jita-jita ko bayanan da ba a tabbatar da sahihancinsu ba yayin da ake jiran sakamakon binciken hukumomi.
