
Jam’iyyar APC reshen Jihar Jigawa ta dakatar da dan Majalisar Tarayya mai wakiltar mazabar Auyo, Hadejia da Kafin Hausa, Hon. Ibrahim Usman Kamfani Auyo, tare da wasu jiga-jigan yan tarakara a jihar
Cikin sanarwar da Shugaban APC na Jihar Jigawa, Hon. Ahmed Garba MK ya sanya wa hannu ranar Lahadi 31 Mayu 2026.
Sanarwar ta bayyana cewa an dauki matakin ne bayan korafe-korafe da rahotannin da suka shafi zargin shiga ayyukan da suka saba wa jam’iyya da kuma haddasa rashin jituwa a tsakanin ƴaƴan jam’iyyar
APC ta ce, zarge-zargen sun shafi wasu abubuwan da suka faru a garin Auyo a ranar 26 ga Mayun 2026, wadanda jam’iyyar ta ce na iya ɓata mata suna da haddasa rabuwar kai a cikinta.
Sauran da aka dakatar sun hada da Aisha Adamu Auyo, Yargabi Babannan Auyo, Musa Idris Zabarau, Ibrahim Ayama, Saje Hadiyau da Sani Abdullahi Hadiyau.
Sanarwar ta ce dakatarwar za ta ci gaba da aiki har sai an kammala bincike tare da mika rahoton kwamitin ladabtarwa na jam’iyyar.
A cikin wani faifan bidiyo dai an hangi ɗan majalisar na gugar zana tare da miƙa saƙo irin na siyasa yana mai cewa, “Ko PDP da ta cika sai da ta danna bindiga, to mu ma tamu tana nan tafe. Muna nan a Jam’iyyar APC domin kayanmu ce…”
