Hukumar kula da kere-kere da kayayyakin kimiyya ta ƙasa, National Agency for Science and Engineering Infrastructure (NASENI), ta kaddamar da shirin tallafin makamashi mai dorewa a jihar Kano State, da nufin rage matsalar karancin makamashi da inganta rayuwar al’umma.
Shirin, wanda aka fara da matakin farko, zai mayar da hankali ne kan rarraba murhunan girki na zamani masu tsafta da kuma na’urorin samar da hasken rana (sola) ga kimanin magidanta 2,000.
Da yake jawabi a wajen kaddamarwar, Shugaban NASENI, Khalil Halilu, ya bayyana cewa shirin zai taimaka wajen rage sare itatuwa, kare lafiyar mata da yara, tare da samar da ingantaccen wutar lantarki ga gidaje da masu kananan sana’o’i.
Ya ce, “Wannan shiri na kawo mafita kai tsaye ga kalubalen rayuwa ta yau da kullum, musamman a bangaren makamashi.”
A nata bangaren, Ministar Masana’antu, Kasuwanci da Zuba Jari, Jumoke Oduwole, ta bayyana shirin a matsayin wani bangare na manufofin gwamnatin Bola Ahmed Tinubu na bunkasa masana’antu, samar da ayyukan yi da kuma karfafa amfani da kayayyakin cikin gida.
Ta kuma bukaci wadanda za su amfana da shirin da su yi amfani da kayan yadda ya kamata domin bunkasa sana’o’insu da inganta rayuwa.
An gudanar da bikin kaddamar da shirin ne a Kano, inda jami’an suka bayyana aniyar fadada shi zuwa sauran jihohin kasar nan nan gaba.
Wasu daga cikin wadanda suka ci gajiyar tallafin sun nuna godiya ga gwamnatin tarayya, tare da alkawarin amfani da kayan yadda ya dace domin inganta rayuwarsu.

