
Daga Brown Pigeon Media
Alhini da jimami sun mamaye ma’aikata da masu sauraron Gidan Radio Kano sakamakon rasuwar shugabar sashen Radio Kano FM, Hajiya Habiba Abubakar Balarabe, wadda ta rasu a daren ranar Laraba bayan fama da gajeriyar jinya.
Marigayiya Habiba Abubakar Balarabe ta kasance fitacciyar ma’aikaciya a Gidan Radio Kano, inda ta yi aiki a sassa daban-daban na tashoshin AM da FM.
Kafin rasuwarta, ta riƙe muƙamin Shugabar Sashen Shirye-shirye na Radio Kano AM, kafin daga bisani aka mayar da ita Daraktar Radio Kano FM.
Haka kuma, marigayiyar ta shahara wajen karanta labarai da gabatar da shirye-shirye daban-daban da suka taimaka wajen wayar da kan al’umma da bunƙasa harkokin yaɗa labarai a jihar Kano.
Kano first

Rasuwarta ta haifar da alhini a tsakanin shugabanni, ma’aikata da masu sauraro, inda ake ci gaba da miƙa saƙonnin ta’aziyya ga iyalanta da daukacin al’ummar gidan Radio Kano.
Ana sa ran za a ci gaba da tunawa da Hajiya Habiba Abubakar Balarabe bisa jajircewarta, ƙwarewarta da kuma gudunmawar da ta bayar wajen ci gaban aikin yaɗa labarai.
Allah Ya jikanta da rahama, Ya gafarta mata kura-kuranta, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarta. Ameen.
by Rukayya Maida
