
Daga Mohammed Babagana Abubakar
A yanayin siyasar dimokuraɗiyya da ke ci gaba da sauyawa a Najeriya, a yau ana auna ingancin shugabanci ne ba da yawan jawabai ko alkawuran siyasa ba, sai da irin tasirin da gwamnati ke yi kai tsaye a rayuwar al’umma. A Arewacin Najeriya, inda jihohi ke fuskantar ƙalubale masu yawa a fannoni kamar ilimi, lafiya, ababen more rayuwa da tsaro, ana ƙara kallon shugabanci ne ta fuskar ikon samar da sakamako mai ma’ana. A Jihar Kano kuwa, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya fito a matsayin jagoran da ke ƙoƙarin sake fasalta ma’anar shugabanci ta hanyar fifita hidima ga jama’a fiye da son kai.
Tun bayan hawansa mulki, Gwamna Yusuf ya mayar da hankali kan aiwatar da manufofi maimakon shiga hayaniyar siyasa da rigingimun jam’iyyanci. Yayin da wasu shugabanni kan ɓata lokaci wajen mayar da martani ga cece kuce da takun sakar siyasa, gwamnatin Kano ta zaɓi mayar da hankali kan magance matsalolin ci gaba da suka shafi al’ummar jihar. Wannan tsari ya taimaka wajen gina gwamnati mai fifita cigaban cibiyoyi da walwalar jama’a sama da muradun siyasa na kashin kai.
Babban misali na wannan salon shugabanci shi ne yadda gwamnatin ta zuba jari sosai wajen bunƙasa albarkatun ɗan Adam. Da yake fahimtar cewa ilimi shi ne ginshiƙin ci gaba mai ɗorewa, gwamnan ya ayyana dokar ta ɓaci a fannin ilimi tare da tabbatar da hakan ta hanyar ware kuɗaɗe masu yawa a kasafin kuɗi. An ware Naira biliyan 432.4 ga ilimi, wanda ya kai kashi 29.4 cikin ɗari na kasafin jihar, adadin da ya zarce ma’aunin kashi 26 cikin ɗari da Hukumar UNESCO ke ba da shawara.
Wannan ware kuɗaɗen ba wai kawai lambobi ba ne, illa wata dabarar tabbatar da adalci da inganta ilimi a dukkan sassan jihar. Ana gina ɗaruruwan sabbin azuzuwa, ana gyaran dubban ɗakunan karatu da makarantu, yayin da aka ɗauki tare da inganta matsayin malamai sama da 8,000 domin ƙarfafa ingancin koyarwa. Haka kuma, gwamnatin ta ci gaba da tallafa wa shirye shiryen bayar da guraben karatu a gida da ƙasashen waje ga ɗalibai marasa galihu, domin ba su damar cimma burinsu na ilimi.
A bangaren lafiya ma, gwamnatin ta nuna irin wannan jajircewa. An ware Naira biliyan 214.8 ga fannin lafiya domin sabunta cibiyoyin kiwon lafiya da kuma faɗaɗa damar samun ingantattun ayyukan lafiya ga jama’a. Ana inganta cibiyoyin lafiya na matakin farko, tare da mayar da wasu zuwa cikakkun asibitocin gwamnati. Haka kuma, shirin kula da mata masu juna biyu da yara kyauta ya ci gaba da rage wa iyalai marasa ƙarfi nauyin kashe kuɗaɗen lafiya. Waɗannan matakai na nuna yadda gwamnatin ke kallon lafiya da ilimi a matsayin haƙƙin jama’a, ba wata ni’ima ta siyasa ba.
Kano first

Ci gaban ababen more rayuwa ma ya zama ɗaya daga cikin manyan nasarorin gwamnatin. A dukkan ƙananan hukumomi 44 na jihar, ana gudanar da ayyukan gina da gyaran hanyoyi domin haɗa birane da ƙauyuka. Waɗannan ayyuka ba wai kawai suna sauƙaƙa zirga zirga ba ne, har ma suna taimakawa kasuwanci, bunƙasa tattalin arziki, da sauƙaƙa kai kaya zuwa kasuwanni. Irin wannan nasara ce ta sa aka karrama Gwamna Yusuf da lambar yabo ta Infrastructure Governor of the Year a taron Africa International Housing Show.
Tsaro kuwa ya kasance wani ginshiƙi mai muhimmanci a tsarin mulkinsa. Kano na ci gaba da kasancewa ɗaya daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya a Najeriya, sakamakon haɗin gwiwar gwamnati da hukumomin tsaro da kuma aiwatar da shirye shiryen tsaro na al’umma. Maimakon dogaro kacokan da hanyoyin tsaro na gargajiya, gwamnatin ta rungumi dabarun rigakafi da gyaran hali domin magance tushen matsalolin rashin tsaro.
Shirye shirye irin su Safe Corridor Initiative suna taimakawa wajen jawo matasa daga miyagun ayyuka da samar musu da hanyoyin rayuwa masu inganci. Haka kuma, rundunar Kano State Neighbourhood Watch Corps ta ƙara ƙarfafa sa hannun al’umma wajen tsaron unguwanninsu ta hanyar haɗa dubban matasa cikin tsarin kula da tsaro na cikin gida.
Idan aka haɗa dukkan waɗannan nasarori, ana iya cewa gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta bayar da wani sabon darasi ga Arewacin Najeriya. Ta nuna cewa idan gwamnati ta mayar da hankali kan hidima ga jama’a, zuba jari a ilimi da lafiya, da kuma samar da mafita mai ɗorewa ga matsalolin al’umma, za a iya samun ci gaba mai ma’ana duk da ƙalubalen siyasa da tattalin arziki.
Yayin da jihar ke ci gaba da tafiya a kan wannan tafarki na ci gaba, muhimmancin wannan salon shugabanci ba zai tsaya ga yawan ayyukan da aka kammala ko kuɗaɗen da aka ware ba. Maimakon haka, zai kasance a cikin al’adar shugabanci da ake gina wa Kano al’adar da ta fifita hidima fiye da son rai, gaskiya fiye da hayaniya, da ci gaba fiye da rarrabuwar kawuna. A zamanin da jama’a ke neman sakamako maimakon alkawura, wannan na iya zama babbar nasarar da za ta daɗe tana bayyana tarihin wannan gwamnati.
