Daukaka Ta Allah Ce: Hakikanin Gwagwarmayar Siyasa da Sakamakonta
Daga: Mohammed Babagana Abubakar
Mail: aunogitalabuba@gmail.com
A cikin tafiyar rayuwa da siyasa, akwai wata gaskiya guda daya da ba ta taba sauyawa: Daukaka da mulki na Allah ne, Shi yake bayar da su ga wanda ya so, a lokacin da ya so. Duk mai ikirarin cewa shi ne ya gina wani, ko kuma shi ne silar daukakar wani ba tare da yardar Ubangiji ba, yana taba dayan siffofin Mahalicci.
Gwagwarmayar Da Aka Yi: Shaidar Tarihi
Nasarar da aka samu a jihar Kano, wadda ta kai ga hawan His Excellency, Gwamna Abba Kabir Yusuf, ba nasarar mutum daya ba ce; nasara ce ta jini, gumi, da sadaukarwar dubban mutane wadanda suka amince da canji. A cikin wannan sahun, akwai jarumai irin su Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, wadanda suka sadaukar da lokacinsu, dukiyarsu, da kwarewarsu wajen ganin wannan buri ya cika.
Ba bukatar fada ba ne, domin ayyuka sun riga sun yi magana. Wanda ya yi aiki tukuru don ganin nasarar gwamnati, kishin al’umma ne ya koro shi, ba wai neman abincin yau da kullum ba. Maganar cewa wani ya taimaki wani da abinci, magana ce da ta saba wa tarbiyyar addini da ta al’ada, domin hannun da ya bayar ya kamata ya manta, ballantana idan aka duba cewa kowa ma bawa ne a gaban Allah.
Siyasa ba ta gadara ba ce, siyasa ta karbuwa ce a wurin mutane. Idan Allah ya sanya mutum ya zama silar nasara a wani gari ko jiha da ba tasa ta haihuwa ba (kamar yadda aka karbi shawarwari da gudunmawar wasu a Kano), wannan wata babbar baiwa ce da ke nuna cewa mutumin yana da tasiri da kwarewa.
Abin takaici ne yadda wasu suke ganin kamar su ne “iyayen gidan” siyasa wadanda ba a isa a yi babu su ba. Kundin tsarin mulkin Najeriya da ma tsarin dimokuradiyya sun ba kowa damar bayyana ra’ayinsa da kuma ba da gudunmawa. Duk wanda ya yi ikirarin shi ya yi wa Gwamna Abba aikin da shi kansa gwamnan bai yi wa kansa ba, to ya kamata ya sani cewa Allah ne ya karbi wannan aikin, ba wai domin dabarar wani mutum ba.
Kwamared Ibrahim Waiya mutum ne mai natsuwa, wanda ya san mutuncin kansa da na magabata. Martaninsa ba na zagi ba ne, face na godiya ga Allah da ya nuna masa wannan rana. Siyasa takaitacciya ce, amma mutunci madawwami ne.
Mutum baya daga mutum sai Allah.
Gwagwarmaya tana bukatar hadin kai, ba gori ba.
Kishin Kano ya kamata ya zama gaba da kishin kai.
Allah ya taimaki jihar Kano, ya kuma sa mu gama da duniya lafiya.