
Mambobin Majalisar Wakilai ta kasa sunyi Kira ga dukkan Ma’aikatun Gwamnati (MDAs) da su daina ƙin karɓar yan bautar kasa na NYSC da ake tura musu domin yin hidimar ƙasa na wajibi na shekara guda.
Wannan matsayar ta biyo bayan wani kudiri da ɗan majalisa Rodney Ebikebina Ambaiowei ya gabatar a zaman majalisar da aka yi a ranar Alhamis, inda ya nuna damuwa kan yadda wasu cibiyoyin gwamnati ke ƙin karɓar masu hidimar ƙasa, lamarin da ke hana su samun ƙwarewar aiki da kuma gudummawa ga ci gaban ƙasa.
Ya bayyana cewa wannan hali na jefa matasa cikin matsala, yana kuma sa su fuskanci barazanar amfani da su ta hanyar kamfanoni masu zaman kansu, har ma da wasu lokuta na iya kai su ga shiga ayyukan da ba su dace ba saboda rashin aikin yi. Ya kuma ce kin karɓar su ɓarna ne ga kuɗaɗen gwamnati, domin ana ci gaba da biyan su alawus duk da cewa ba a ba su aiki yadda ya kamata ba.
Majalisar ta amince da kudirin, inda ta bukaci dukkan MDAs ciki har da Majalisar Tarayya da su daina ƙin karɓar masu hidimar ƙasa, su kuma tsara ayyukan da za su ba su damar shiga cikin harkokin aikinsu. Haka kuma, ta umarci Kwamitin Matasa na Majalisar da ya yi aiki tare da Darakta Janar na NYSC domin samar da tsarin da zai inganta yadda za a rika amfani da ƙwarin gwiwar masu hidimar ƙasa a lokacin bautar ƙasa.
