Close Menu
  • Home
  • News
    • National
    • International
  • Business
  • Education
  • Featured
  • Health
  • Politics
  • Sports
  • Videos
  • More
    • About Us
    • Contact Us
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram
Facebook Instagram TikTok
BROWN PIGEON MEDIA
SUBSCRIBE
  • Home
  • News
    1. National
    2. International
    3. View All

    FEDERAL GOVERNMENT SUSPENDS PROPOSED WAEC, NECO REGISTRATION FEE HIKE

    July 13, 2026

    FG: FANNIN MA’ADANAI YA JAWO JARIN DALA BILIYAN 3 CIKIN SHEKARU UKU

    June 18, 2026

    GWAMNATIN TARRAYYA TA MUSANTA SHIRIN SOKE HUKUMAR NBAIS

    June 18, 2026

    DEMOCRACY DAY SPEECH: OUR GENERATION MUST SECURE PROSPERITY 

    June 12, 2026

    Senator Barau Reaffirms ECOWAS Parliament’s Commitment to Regional Unity at Commissioning of New ECOWAS Headquarters

    July 3, 2026

    DA DUMI-DUMI: Starmer ya yi Murabus Daga Mukamin Firaministan Birtaniya

    June 22, 2026

    NETANYAHU YA SHA ALWASHIN HANA IRAN MALLAKAR MAKAMIN NUKILIYA

    June 13, 2026

    Girgizar Ƙasa Mai Ƙarfi Ta Hallaka Mutane a Philippines, Ana Fargabar Tsunami a Wasu Ƙasashe

    June 8, 2026

    CELEBRATING EXCELLENCE BEYOND POLITICS: WHY COMRADE IBRAHIM ABDULLAHI WAIYA DESERVES THE WINSEC AWARD

    August 5, 2026

    FREQUENTLY ASKED QUESTIONS (FAQ) ABOUT DSP BARAU I. JIBRIN… AND THEIR ANSWERS

    August 5, 2026

    WAIYA PLEDGES COLLABORATION WITH EX-COUNCILLORS’ FORUM, NORTH WEST APC WOMEN MEDIA GROUP AS BOTH DECLARE SUPPORT FOR GOVERNOR ABBA

    August 4, 2026

    Ibrahim Abdullahi Waiya: Leadership Defined by Focus, Vision and Service

    August 4, 2026
  • Business

    KASEDA TA GUDANAR DA SHIRIN WAYAR DA KAI GA MSMEs KAN KA’IDOJIN NAFDAC A JIHAR KATSINA

    June 12, 2026

    Dangote Industrialising Africa– NCCIMA DG

    May 17, 2026

    INEC TA BUKACI MASU RIJISTAR KATIN ZABE A KANO DA SU JE SU DUBA SUNAYENSU

    April 27, 2026

    KANO TO HOST NATIONAL LAUNCH OF ECoN INITIATIVE, SET TO DRIVE INNOVATION AND INDUSTRIAL GROWTH IN NORTH-WEST

    April 16, 2026

    NewsNigeria’s Inflation Rate Climbs to 15.38% in March

    April 16, 2026
  • Education

    KANO PRIVATE SCHOOLS BOARD SUSPENDS 10% STATUTORY TAX PENDING FRESH ASSESSMENT

    August 1, 2026

    2027 PRESIDENCY: TINUBU DECLARES UNIVERSITY DEGREE, LEAVES OUT PRIMARY, SECONDARY EDUCATION

    August 1, 2026

    Governor Abba Kabir Yusuf, Education Minister Commission New Girls’ Secondary School in Kumbotso

    July 22, 2026

    Gwamnatin Kano Ta Umarci Jami’ar Azman Ta Gabatar da Takardun Gini Ko Ta Fuskanci Rufe Makarantar

    June 23, 2026

    Kano Govt Reaffirms Commitment to Children’s Welfare at International Children’s Day Celebration

    June 14, 2026
  • Featured

    Kano State Government Organises Two-Day Retreat for Online Media Publishers in Jigawa

    January 15, 2026

    Former Kano APC Councilors Hold Special Prayers for Governor Abba Kabir Yusuf

    October 27, 2025

    Mustapha Salisu Makes Azerbaijan Move

    September 9, 2025

    Delta 2025 NYG: Team Kano Finish 9th With 14 Medals

    September 8, 2025

    Kano Government Clarifies Position on Elders Council, Backs Its Own Initiative

    September 7, 2025
  • Health

    NORTH-WEST DEVELOPMENT COMMISSION TEAMS UP WITH DALA ORTHOPAEDIC HOSPITAL TO EASE MEDICAL COSTS

    August 1, 2026

    Kano Government Targets Maternal Mortality with 484 New Mini-Ambulances for Rural Wards

    June 19, 2026

    Gwamnatin Kano Ta Sayi Ƙananan Motocin Asibiti 484 Domin Taimaka wa Mata Masu Juna Biyu – Kwamishinan Lafiya

    June 19, 2026

    SHAYAR DA NONON UWA ZALLA NA KARE YARA DAGA CUTUTTUKA — KWAMISHINAN LAFIYA

    June 16, 2026

    Hukumar Kula da Asibitocin Kano Ta Tsaurara Matakai Kan Rashin Zuwa Aiki bisa Jadawalin Ayyuka

    June 11, 2026
  • Politics

    SANATA RUFAI SANI HANGA YA FICE DAGA JAM’IYYAR NDC

    August 3, 2026

    KWANKWASIYYA-SHEKARAU UNITY FORUM REBRANDS, DECLARES TOTAL SUPPORT FOR GOVERNOR ABBA KABIR YUSUF AHEAD OF 2027

    July 21, 2026

    Governor Abba Kabir Yusuf Declares Murtala Sule Garo as 2027 Deputy Governorship Running Mate

    July 13, 2026

    APC zata Bayyana Shettima a Matsayin Mataimakin Takarar Tinubu na 2027

    July 10, 2026

    TSOFAFFIN SHUGABANNIN ƘANANAN HUKUMOMI DA KANSILOLI SUN BAYYANA GOYON BAYANSU GA GWAMNA ABBA KABIR YUSUF

    July 10, 2026
  • Sports

    Bichi First FC Unveils Abubakar Senior as New Technical Adviser

    September 11, 2025

    Mustapha Salisu Makes Azerbaijan Move

    September 9, 2025

    Delta 2025 NYG: Team Kano Finish 9th With 14 Medals

    September 8, 2025

    If Super Eagles Fail to Qualify for World Cup, Nigerians Will Not Forgive Us – Ahmed Musa

    September 6, 2025

    Super Falcons striker and six-time African Women’s Footballer of the Year, Asisat Oshoala, has completed her move from Bay FC to Saudi Women’s Premier League side Al Hilal

    September 3, 2025
  • Videos
  • More
    • About Us
    • Contact Us
    • Privacy Policy
BROWN PIGEON MEDIA
Home » DAGA NAƊAƊƊE ZUWA MAI TAYAR DA HANKALI: BINCIKEN GASKIYAR MANUFOFIN DA KE BAYAN HARE-HAREN GALADIMA GA GWAMNA YUSUF DA DSS
Politics

DAGA NAƊAƊƊE ZUWA MAI TAYAR DA HANKALI: BINCIKEN GASKIYAR MANUFOFIN DA KE BAYAN HARE-HAREN GALADIMA GA GWAMNA YUSUF DA DSS

Brown Pigeon MediaBy Brown Pigeon MediaMarch 2, 20265 Mins Read
Facebook Twitter WhatsApp Telegram Email Copy Link

 

Daga Mohammed Babagana Abubakar

 

 

A dandalin siyasar Nijeriya, akwai wasu ‘yanwasa da suka kware wajen abin da masu nazari ke kira dabarar kawar da hankali: wato haifar da hayaniya mai yawa kan zargin rashin adalci a daidai lokacin da tasirinsu a siyasa ke dusashewa. Kalaman da Alhaji Buba Galadima ya rika yi a baya-bayannan kan Mai Girma Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf, da kuma Daraktan Hukumar Tsaro ta DSS a Kano, misali ne karara na wannan salo. Zarge-zargen rashin adalci da kuma kama masu adawa da gwamnati da cewar ana farautarsu na nuna tamkar jihar na cikin rikici. Amma idan aka yi duba na gaskiya da idon basira, labarin ya sha bamban matuƙa.

 

Ba abin mamaki ba ne cewa hare-haren Galadima sun ƙaru nan take bayan cire shi daga kujerar Shugaban Majalisar Gudanarwa ta Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano (Kano State Polytechnic) a watan Fabrairu 2026. Gwamna Yusuf, bisa manufarsa ta Kano First Agenda, wani tsarin gudanar da mulki da ke mayar da hankali kan inganta cibiyoyi da fifita ci gaban Kano, ya sauke Galadima daga mukamin, yana mai nuni da bukatar inganta aiki da sake farfaɗo da cibiyar. Daga bisani, aka naɗa Sarkin Gaya, Alhaji Aliyu Abdulkadir, wanda darajarsa da kusancinsa da al’umma suka dace da burin sake fasalin da Gwamnan ke nema.

 

Ga mutumin da ya riƙe babban mukami a wata jiha da ba jiharsa ba, abin da ya fi dacewa shi ne barin mukamin cikin mutunci da kima. Amma maimakon haka, Galadima ya zaɓi ramuwar gayya. Kamfen dinsa na kafafen yaɗa labarai, wanda ke ƙaruwa a kowace hira, ba dabi’ar mai fafutukar dimokuraɗiyya ba ce. Dabi’a ce ta wanda aka cire masa damar cin moriyar mukami, kuma yake son ya sa a biya farashin siyasa kan hakan.

 

Zarge-zargen da Galadima ya yi, ciki har da batun kama wani mai shirin rediyo da kuma bayyana matakan jami’an tsaro a matsayin tsangwama ta siyasa, ƙoƙari ne na karkatar da gaskiyar tsarin mulki da aikace-aikacen gwamnati a Kano. A halin yanzu, Kano na tafiya a cikin yanayi mai sarkakiya ta fuskar tsaro da siyasa, musamman ma bayan da Gwamnan ya yi sauyin sheka ta siyasa zuwa APC, wanda ya buƙaci daidaita siyasar jihar cikin sabon yanayin ikon ƙasa. A irin wannan yanayi, ayyukan DSS suna gudana ne bisa dokar tarayya, hurumin hukuma, da kuma sahihan korafe-korafe, ba bisa umarnin siyasa ba.

 

‘Yancin faɗin albarkacin baki, wanda Sashe na 39 na Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Nijeriya ya tanada, hakki ne da gwamnatin Gwamna Yusuf ta mutunta. Amma babu wani sashe na kundin da ke bai wa mutum damar amfani da kafafen yaɗa labarai don tunzura rikici, yada ƙarya da aka tabbatar, ko aikata laifukan da Dokar Yaki da Laifukan Yanar Gizo (Cybercrime Act 2015) ta haramta. Idan jami’an tsaro suka gayyaci wani domin amsa tambayoyi bisa sahihancin korafe-korafe a ƙarƙashin wannan doka, wannan aiki ne na bin doka da oda. Kiransa da “garkuwa ta siyasa” ba fafutukar dimokuraɗiyya ba ce; misali ne na ɓata suna da gangan.

 

Yayin da Galadima ke gina labarin tsangwama, gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf na gina abin da ya fi muhimmanci, rikodin mulki. Gwamnatin ta fara gyaran manyan makarantun gaba da sakandare na jihar, tana magance matsalolin da suka daɗe suna faruwa. Ta ɗauki matakan biyan basussukan garatuti ga ma’aikatan gwamnati da suka yi ritaya, alƙawarin da gwamnatocin baya suka kasa cikawa. Haka kuma, ta fara rushe tsarin siyasar ubangida, inda aka daɗe ana mayar da cibiyoyin gwamnati tamkar mallakin masu iko maimakon al’umma.

 

Wannan rushewar tsarin siyasar gata ne da ke bayyana ainihin dalilin da ke bayan kamfen ɗin Galadima. Ba wai ya ƙi tsarin mulkin Gwamna Yusuf ba ne; abin da yake ƙi shi ne sabon yanayin da ba ya ba da tabbacin samun mukamai da tasiri bisa alaƙar siyasa kaɗai. Cire shi daga kwalejin ba kawai sauyin aiki ba ne; alama ce cewa tsoffin tsare-tsare sun ƙare. Martaninsa kuwa shi ne ƙoƙarin nuna cewa irin waɗannan matakai suna da tsada a siyasa. Amma Gwamna Yusuf da gwamnatinsa dole ne su ci gaba da tafiya ba tare da gezau ba.

 

Al’ummar Kano ba kawai kallo suke ba, kuma ba za a yaudare su ba. Suna da wayewar siyasa da tarihin fahimta mai zurfi, kuma suna iya bambance tsakanin fafutukar dimokuraɗiyya ta gaskiya da siyasar ƙorafi wadanda suka rasa madogara. Galadima ba ya yaƙi ne don talakawan Kano; yana yaƙi ne don mukami da aka raba shi da shi, gata da aka janye, da tasirin siyasa da ya rasa. Wannan haƙƙinsa ne. Amma ya kamata a kira shi da sunansa na gaskiya.

 

An zaɓi Gwamna Abba Kabir Yusuf ne domin ya yi mulki bisa muradun al’ummar Kano, ba don kiyaye damar gata ta wasu ba. Gwamnatinsa, DSS, da dukkan cibiyoyin da ke aiki bisa hurumin kundin mulki dole ne su ci gaba da mai da hankali kan wannan manufa, ba tare da shagaltuwa da hayaniyar masu jin zafin rasa gata ba. Makomar Kano za ta ginu ne da nagartaccen mulki, aiki tukuru, da rikon amana, ba kan ƙorafe-ƙorafen da aka ƙirƙira domin dawo da tsohuwar daula ba.

 

 

GAME DA MARUBUCIN

Mohammed Babagana Abubakar mai sharhi ne kan siyasa da nazarin al’amuran mulki, mai sha’awar batutuwan rikon amana, ingantaccen shugabanci, da ci gaban dimokuraɗiyya a Kano da Arewacin Nijeriya.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email VKontakte WhatsApp Copy Link
Previous ArticleIran Ta Tabbatar Da Kisan Ali Khamenei Da Iyalansa By Mutawakkilu
Next Article Ba boyayyen abu ba ne cewa siyasar Kano ba ta taɓa zama al’ada ba

Related Posts

SANATA RUFAI SANI HANGA YA FICE DAGA JAM’IYYAR NDC

August 3, 2026

KWANKWASIYYA-SHEKARAU UNITY FORUM REBRANDS, DECLARES TOTAL SUPPORT FOR GOVERNOR ABBA KABIR YUSUF AHEAD OF 2027

July 21, 2026

Governor Abba Kabir Yusuf Declares Murtala Sule Garo as 2027 Deputy Governorship Running Mate

July 13, 2026

APC zata Bayyana Shettima a Matsayin Mataimakin Takarar Tinubu na 2027

July 10, 2026

TSOFAFFIN SHUGABANNIN ƘANANAN HUKUMOMI DA KANSILOLI SUN BAYYANA GOYON BAYANSU GA GWAMNA ABBA KABIR YUSUF

July 10, 2026

Kano Information Commissioner Engages Broadcast Commentators to Strengthen Public Information

June 30, 2026
Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • Telegram
  • WhatsApp
Latest Posts

CELEBRATING EXCELLENCE BEYOND POLITICS: WHY COMRADE IBRAHIM ABDULLAHI WAIYA DESERVES THE WINSEC AWARD

By Brown Pigeon MediaAugust 5, 2026

By Comrade Najeeb Nasir Ibrahim In every society, there are individuals whose dedication to…

FREQUENTLY ASKED QUESTIONS (FAQ) ABOUT DSP BARAU I. JIBRIN… AND THEIR ANSWERS

August 5, 2026

WAIYA PLEDGES COLLABORATION WITH EX-COUNCILLORS’ FORUM, NORTH WEST APC WOMEN MEDIA GROUP AS BOTH DECLARE SUPPORT FOR GOVERNOR ABBA

August 4, 2026

Ibrahim Abdullahi Waiya: Leadership Defined by Focus, Vision and Service

August 4, 2026

KANO RECORDS REVENUE SURGE AS DIGITAL LAND SYSTEM RAISES MONTHLY EARNINGS TO ₦750 MILLION

August 3, 2026
© 2026 Brown Pigeon Media. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.