Close Menu
  • Home
  • News
    • National
    • International
  • Business
  • Education
  • Featured
  • Health
  • Politics
  • Sports
  • Videos
  • More
    • About Us
    • Contact Us
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram
Facebook Instagram TikTok
BROWN PIGEON MEDIA
SUBSCRIBE
  • Home
  • News
    1. National
    2. International
    3. View All

    DEMOCRACY DAY SPEECH: OUR GENERATION MUST SECURE PROSPERITY 

    June 12, 2026

    Majalisar wakilai Ta Amince Da Kudirin Kafa Ƴansandan Jihohi 

    June 11, 2026

    COURTESY AND COLLABORATION VISIT BY THE INDONESIAN HAJJ FINANCIAL MANAGEMENT AGENCY (BPKH) TO NAHCON

    June 7, 2026

    Ganduje, NGF chairman join special democracy day prayer as FG pledges stronger democracy

    June 6, 2026

    NETANYAHU YA SHA ALWASHIN HANA IRAN MALLAKAR MAKAMIN NUKILIYA

    June 13, 2026

    Girgizar Ƙasa Mai Ƙarfi Ta Hallaka Mutane a Philippines, Ana Fargabar Tsunami a Wasu Ƙasashe

    June 8, 2026

    Yan Sanda a ƙasar Turkiyya Sun Gano Baƙin Haure 30 da aka Boye a Cikin Wata Tankar Mai

    June 5, 2026

    Saudiyya Ta Raba Alƙur’ani Miliyan 1.9 Ga Alhazan Bana

    June 2, 2026

    The Prophet’s Mosque, Al-Rawdah, and the Serenity That Fills the Visitor’s Heart

    June 14, 2026

    A STATEMENT THAT CASTS DOUBT ON PETER OBI’S FITNESS TO BE PRESIDENT 

    June 14, 2026

    The Rule of Law vs. Political Expediency: The Security Risks of Bypassing Judicial Processes

    June 14, 2026

    Mulkin Doka da Maslahar Siyasa: Barazanar Tsaro da ke Tattare da Kauce wa Hanyoyin Shari’a

    June 14, 2026
  • Business

    KASEDA TA GUDANAR DA SHIRIN WAYAR DA KAI GA MSMEs KAN KA’IDOJIN NAFDAC A JIHAR KATSINA

    June 12, 2026

    Dangote Industrialising Africa– NCCIMA DG

    May 17, 2026

    INEC TA BUKACI MASU RIJISTAR KATIN ZABE A KANO DA SU JE SU DUBA SUNAYENSU

    April 27, 2026

    KANO TO HOST NATIONAL LAUNCH OF ECoN INITIATIVE, SET TO DRIVE INNOVATION AND INDUSTRIAL GROWTH IN NORTH-WEST

    April 16, 2026

    NewsNigeria’s Inflation Rate Climbs to 15.38% in March

    April 16, 2026
  • Education

    Kano Govt Reaffirms Commitment to Children’s Welfare at International Children’s Day Celebration

    June 14, 2026

    The Two Faces of Kano’s Democracy: Political Turbulence and Grassroots Progress Under Abba Kabir Yusuf

    June 12, 2026

    Kebbi Expands Early Childhood Education with N1.59bn Investment

    June 12, 2026

    ABU most Grateful to UNESCO-ICHEI for Sustained Support – VC

    June 12, 2026

    Turn research into wealth, Deputy Senate President urges universities

    June 11, 2026
  • Featured

    Kano State Government Organises Two-Day Retreat for Online Media Publishers in Jigawa

    January 15, 2026

    Former Kano APC Councilors Hold Special Prayers for Governor Abba Kabir Yusuf

    October 27, 2025

    Mustapha Salisu Makes Azerbaijan Move

    September 9, 2025

    Delta 2025 NYG: Team Kano Finish 9th With 14 Medals

    September 8, 2025

    Kano Government Clarifies Position on Elders Council, Backs Its Own Initiative

    September 7, 2025
  • Health

    Hukumar Kula da Asibitocin Kano Ta Tsaurara Matakai Kan Rashin Zuwa Aiki bisa Jadawalin Ayyuka

    June 11, 2026

    Race Against Time: KSCHMA Rapid Response Team Secures Emergency Surgery for Accident Victim at Sir Muhammad Sunusi Specialist Hospital

    June 9, 2026

    Zulum Sets 60-Day Deadline for 400-Bed Teaching Hospital, Orders Completion of Orthopaedic Hospital in Four Months

    June 6, 2026

    ABU TEACHING HOSPITAL COMMEMORATES WORLD HYPERTENSION DAY 2026.

    June 6, 2026

    Zulum Directs Distribution of Free Cholera Drugs, Medical Consumables to Health Facilities

    June 1, 2026
  • Politics

    Peter Obi’s Nnamdi Kanu Promise: A Risky Political Calculation Nigerians Must Question

    June 14, 2026

    PETER OBI YAYI ALKAWARIN SAKIN NNAMDI KANU IDAN YA ZAMA SHUGABAN KASA

    June 13, 2026

    Gwamnan Kano Ya Yi Sabbin Naɗe-naɗe da Sauye-sauyen Mukamai Domin Inganta Ayyukan Gwamnati

    June 11, 2026

    Sen. Nakudu Hails INEC’s Restoration Of Aujara State Constituency

    June 11, 2026

    NNPP Ta Zargi Kwankwaso Da Ci Gaba Da Tsoma Baki A Harkokinta Duk Da Ficewarsa

    June 11, 2026
  • Sports

    Bichi First FC Unveils Abubakar Senior as New Technical Adviser

    September 11, 2025

    Mustapha Salisu Makes Azerbaijan Move

    September 9, 2025

    Delta 2025 NYG: Team Kano Finish 9th With 14 Medals

    September 8, 2025

    If Super Eagles Fail to Qualify for World Cup, Nigerians Will Not Forgive Us – Ahmed Musa

    September 6, 2025

    Super Falcons striker and six-time African Women’s Footballer of the Year, Asisat Oshoala, has completed her move from Bay FC to Saudi Women’s Premier League side Al Hilal

    September 3, 2025
  • Videos
  • More
    • About Us
    • Contact Us
    • Privacy Policy
BROWN PIGEON MEDIA
Home » Mulkin Doka da Maslahar Siyasa: Barazanar Tsaro da ke Tattare da Kauce wa Hanyoyin Shari’a
News

Mulkin Doka da Maslahar Siyasa: Barazanar Tsaro da ke Tattare da Kauce wa Hanyoyin Shari’a

Brown Pigeon MediaBy Brown Pigeon MediaJune 14, 20266 Mins Read
Facebook Twitter WhatsApp Telegram Email Copy Link
Mutawakkilu Ibrahim Idris
Mulkin Doka da Maslahar Siyasa: Barazanar Tsaro da ke Tattare da Kauce wa Hanyoyin Shari’a
Mutawakkilu Ibrahim Idris
Mulkin Doka da Maslahar Siyasa: Barazanar Tsaro da ke Tattare da Kauce wa Hanyoyin Shari’a

 

Daga Mohammed Babagana Abubakar

 

Ƙarfin kowace al’umma mai bin tsarin dimokuraɗiyya ba ya ta’allaka ne kawai kan gudanar da zaɓe ko bai wa jama’a damar shiga harkokin siyasa ba, sai dai ya fi karkata ga fifikon mulkin doka. Ƙasar da ake tafiyar da ita bisa doka maimakon son zuciyar mutane suna more zaman lafiya, tabbaci, da kuma amincewar jama’a ga cibiyoyinta. Akasin haka kuwa, idan aka fara mayar da harkokin shari’a ƙarƙashin lissafin siyasa, ginshiƙan dimokuraɗiyya kan fara raunana, tare da jefa tsaron ƙasa cikin haɗari.

 

Wannan muhawara ta sake tasowa ne bayan kalaman da Peter Obi, Dan takar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC), ya yi dangane da ci gaba da tsarewa da kuma gurfanar da shugaban ƙungiyar IPOB, Nnamdi Kanu. Yayin wata ganawa a birnin Washington D.C., Obi ya bayyana cewa tattaunawa da sulhu su ne mafi dacewa wajen samar da zaman lafiya fiye da tsawaita rigingimun shari’a, yana mai cewa babu wani dalili mai ƙarfi da zai sa a ci gaba da tsare Kanu.

 

Duk da cewa kira zuwa ga zaman lafiya da sulhu wani muhimmin bangare ne na tsarin dimokuraɗiyya, wannan batu ya haifar da muhimmiyar tambaya. Shin ya dace a fifita maslahar siyasa a kan hanyoyin shari’a da ke gudana ba tare da raunana mulkin doka ba?

 

Batun ya wuce makomar mutum guda. Abin da ke kan gaba shi ne martabar tsarin shari’ar Najeriya da kuma ƙa’idar cewa dole ne a gudanar da adalci ta hanyoyin kundin tsarin mulki, ba ta hanyar sasancin siyasa ba.

 

Babban abin damuwa na farko shi ne yiwuwar raunana ikon bangaren shari’a. Kotuna an kafa su ne domin fassara doka, yanke hukunci a kan saɓani, da tantance gaskiya ko laifi bisa hujjoji. Amincewar jama’a da kotuna na dogara ne da tabbacin cewa za a mutunta kuma a aiwatar da hukuncinsu. Lokacin da ‘yan siyasa suka fara nuna cewa za a iya kauce wa hukuncin kotu ta hanyar tsoma bakin gwamnati ko yarjejeniyar siyasa, hakan na iya rage amincewar jama’a da tsarin shari’a.

 

A kowace dimokuraɗiyya mai bin kundin tsarin mulki, duk wanda bai gamsu da hukuncin kotu ba yana da hanyoyin neman sauyi ta doka, ciki har da ɗaukaka ƙara da neman sake dubawa. Waɗannan hanyoyi ne da ke tabbatar da cewa an warware sabani cikin tsarin doka. Kauce wa waɗannan hanyoyi domin cimma yarjejeniyar siyasa na aika da saƙo mara kyau cewa sakamakon shari’a ba ya rataye kan hujjoji ko doka, sai dai kan tasirin siyasa.

 

Abu na biyu da ke haifar da damuwa shi ne batun tsaron ƙasa da hana aikata laifi. Hukumomin tsaro, masu gabatar da ƙara, da jami’an shari’a suna kashe lokaci da albarkatu masu yawa wajen bincike da gurfanar da waɗanda ake zargi da aikata laifukan da ke barazana ga zaman lafiyar ƙasa da haɗin kanta. Tsarin shari’a ba wai domin hukunta masu laifi kawai aka samar da shi ba, har ma domin hana wasu aikata irin waɗannan laifuka a gaba.

Kano first

Idan jama’a suka fara ganin cewa wasu da ake zargi ko aka samu da aikata manyan laifuka suna samun sassauci ta hanyar yarjejeniyar siyasa, ƙarfin doka wajen hana laifuka zai ragu. Ƙungiyoyi ko mutane masu korafi ga gwamnati za su iya ɗaukar hakan a matsayin hujjar cewa matsin lamba ko tarzoma na iya kai su ga samun rangwame daga gwamnati. Wannan fahimta na iya ƙara haddasa rashin zaman lafiya maimakon rage shi.

 

Abu na uku shi ne ƙa’idar adalci iri ɗaya ga kowa a ƙarƙashin doka. Najeriya ƙasa ce mai cike da bambance bambancen ƙabila, addini, da yankuna. Domin tabbatar da haɗin kan ƙasa, wajibi ne a aiwatar da doka cikin adalci da daidaito ga kowane mutum da kowane yanki.

 

Duk wata fahimta da ke nuna cewa wasu mutane ko ƙungiyoyi suna samun fifiko saboda tasirinsu na siyasa ko na yanki na iya haifar da jin rashin adalci a tsakanin sauran ‘yan ƙasa. Wannan yanayi na da matuƙar haɗari musamman a ƙasar da ke fuskantar matsalolin tsaro daga yankuna daban daban.

 

Sai dai kuma, waɗannan damuwar ba su kamata a fassara su a matsayin adawa da tattaunawa ba. A tarihin duniya, tattaunawa ta taka muhimmiyar rawa wajen warware rikice rikice da magance korafe korafen siyasa. Zaman lafiya mai ɗorewa na buƙatar tattaunawa, sulhu, da fahimtar juna. Amma ya kamata tattaunawa da mulkin doka su kasance masu cike juna, ba masu takaddama da juna ba.

 

Gwamnati mai bin tsarin dimokuraɗiyya na iya neman sulhu tare da mutunta ‘yancin bangaren shari’a. Shugabanni za su iya ba da shawarar gyare gyare, ƙarfafa zaman lafiya, da magance korafe korafe ba tare da katsalandan ga shari’o’in da ke gudana ko rage martabar kotuna ba.

 

Haka kuma, duk wata tattaunawa kan sulhu dole ne ta yi la’akari da waɗanda tashin hankali da rashin tsaro suka shafa. Dole ne manufofin gwamnati su daidaita tausayi da ɗaukar alhaki, ta yadda za a tabbatar da cewa adalci ya yi wa zaman lafiya da kuma waɗanda suka sha wahala aiki.

 

Yayin da Najeriya ke ci gaba da tafiya a tafarkin dimokuraɗiyya, ƙasar na fuskantar wani babban gwaji. shin za ta ci gaba da tsayawa kan ƙa’idojin kundin tsarin mulki ko kuwa za ta rungumi hanyoyin da suka fi dacewa da maslahar siyasa ta ɗan lokaci? Ko da yake jarabar neman gajeriyar nasara ta siyasa na iya kasancewa mai ƙarfi, sakamakon da zai biyo baya na iya zama mai tsanani.

 

A ƙarshe, mulkin doka dole ne ya ci gaba da kasancewa ginshiƙin shugabanci. Shugabanni kan zo su wuce, amma cibiyoyi su ne ke dorewa. Kare martabar waɗannan cibiyoyi yana da muhimmanci ga dimokuraɗiyya, tsaron ƙasa, zaman lafiyar al’umma, da makomar Najeriya.

 

Ƙasar da ake mulkinta bisa doka ta fi ƙarfi fiye da ƙasar da ake tafiyar da ita bisa maslahar siyasa. Domin Najeriya ta samu zaman lafiya mai ɗorewa da ci gaba mai ma’ana, mutunta hanyoyin kundin tsarin mulki dole ne ya kasance abin da ba za a yi sulhu a kansa ba.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email VKontakte WhatsApp Copy Link
Previous ArticleDialogue or De-escalation? Why Negotiating Convicted Separatist Leaders Could Undermine National Deterrence
Next Article The Rule of Law vs. Political Expediency: The Security Risks of Bypassing Judicial Processes

Related Posts

The Prophet’s Mosque, Al-Rawdah, and the Serenity That Fills the Visitor’s Heart

June 14, 2026

A STATEMENT THAT CASTS DOUBT ON PETER OBI’S FITNESS TO BE PRESIDENT 

June 14, 2026

The Rule of Law vs. Political Expediency: The Security Risks of Bypassing Judicial Processes

June 14, 2026

Dialogue or De-escalation? Why Negotiating Convicted Separatist Leaders Could Undermine National Deterrence

June 14, 2026

SULHU DA MASU RAJIN RABA ƘASA: HANYAR ZAMAN LAFIYA KO BARAZANA GA DOKA?

June 14, 2026

SETTING THE SENATE ABLAZE WITH PERFORMANCE: BARAU JIBRIN’S HISTORIC 42-BILL MASTERPIECE

June 14, 2026
Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • Telegram
  • WhatsApp
Latest Posts

The Prophet’s Mosque, Al-Rawdah, and the Serenity That Fills the Visitor’s Heart

By Brown Pigeon MediaJune 14, 2026

By Abubakar Dangambo Madinah Al-Munawwarah, the radiant city of the Prophet Muhammad (peace be…

A STATEMENT THAT CASTS DOUBT ON PETER OBI’S FITNESS TO BE PRESIDENT 

June 14, 2026

The Rule of Law vs. Political Expediency: The Security Risks of Bypassing Judicial Processes

June 14, 2026

Mulkin Doka da Maslahar Siyasa: Barazanar Tsaro da ke Tattare da Kauce wa Hanyoyin Shari’a

June 14, 2026

Dialogue or De-escalation? Why Negotiating Convicted Separatist Leaders Could Undermine National Deterrence

June 14, 2026
© 2026 Brown Pigeon Media. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.