
Rahotanni sun bayyana cewa wata jami’ar rundunar sojin ruwan Najeriya ta rasu bayan da aka ce an hukunta ta ta hanyar tsayar da ita ƙarƙashin zafin rana a wani sansanin rundunar ruwa da ke jihar Lagos.
An ce lamarin ya faru ne a cibiyar lafiya ta rundunar ruwa da ke Gowon Estate, Ipaja, inda ake zargin wasu manyan jami’ai da tilasta mata tsayuwa cikin rana mai tsanani har ta yanke jiki.
Lamarin ya jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta, inda mutane da dama ke kira ga hukumomin rundunar ruwa da gwamnatin tarayya da su gudanar da bincike mai zurfi domin gano gaskiyar abin da ya faru.
Har zuwa yanzu rundunar sojin ruwan Najeriya ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance kan zargin ba.
