
By Mutawakkilu Ibrahim Idris
Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kano ta sanar da rufe dukkan makarantun firamare da sakandare na gwamnati da masu zaman kansu domin hutun Babbar Sallah ta Eid-el-Kabir. Sanarwar ta fito ne ta hannun Daraktan Wayar da Kai na ma’aikatar, Malam Misbahu Yakasai, a ranar Laraba.
A cewar sanarwar, daliban makarantun kwana za su fara hutun Sallah daga ranar Asabar 23 ga watan Mayu, 2026. An kuma bayyana cewa za su koma makaranta ranar Lahadi 31 ga watan Mayu, 2026 bayan kammala hutun.
Haka zalika, ma’aikatar ta ce makarantun yini za su fara hutun ne daga ranar Juma’a 22 ga watan Mayu, 2026. Za a ci gaba da karatu a makarantun ranar Litinin 1 ga watan Yuni, 2026.
Sanarwar ta bukaci iyaye da masu kula da dalibai su tabbatar sun je karbar ‘ya’yansu daga makarantun kwana a ranar da aka kayyade domin rufe makarantu. Ta kuma nemi su tabbatar da dawo da daliban a kan lokaci lokacin komawa makaranta.
Ma’aikatar ta jaddada muhimmancin bin jadawalin hutun da aka tsara domin kauce wa matsalolin tsaiko wajen komawa karatu. Ta ce ana sa ran dukkan makarantu za su bi umarnin yadda ya kamata.
A cewar jami’an ma’aikatar, hutun na daga cikin shirye-shiryen bai wa dalibai da malamai damar gudanar da bukukuwan Sallah cikin walwala tare da iyalansu. Sun ce hakan zai taimaka wajen karfafa zumunci da hadin kai a tsakanin al’umma.
Sanarwar ta kuma bayyana cewa gwamnati na ci gaba da kokarin inganta harkokin ilimi a jihar tare da tabbatar da yanayi mai kyau ga dalibai da malamai. Ta ce ana sa ran komawa karatu cikin tsari bayan hutun Sallah.
Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Dakta Ali Makoda, ya yi kira ga dalibai su yi amfani da hutun wajen gudanar da abubuwa masu anfani da kuma kiyaye dokoki da tarbiyya. Ya kuma bukaci malamai da iyaye su ci gaba da bai wa yara kulawar da ta dace.
Hakazalika, ya yi wa daukacin al’ummar jihar Kano fatan gudanar da bikin Eid-el-Kabir cikin zaman lafiya, kwanciyar hankali da walwala. Ya ce gwamnatin jihar na addu’ar samun nasara da ci gaba ga al’umma baki daya.
Sanarwar ta zo ne yayin da al’ummar Musulmi ke ci gaba da shirye-shiryen gudanar da bikin Babbar Sallah a sassan Najeriya, inda ake sa ran miliyoyin mutane za su gudanar da bukukuwan cikin farin ciki da annashuwa.
