
Shugaba kasa Bola Tinubu ya yaba wa Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya bisa rawar da take takawa wajen kare ruwan Najeriya, yana mai cewa ta kasance ginshikin tsaron kasar nan ta ruwa.
Shugaba Tinubu ya bayyana haka a wajen bikin cika shekaru 70 na Sojin Ruwa, wanda aka gudanar a bakin teku na Eko Atlantic da ke Legas a ranar Litinin din nan.
A yayin bikin Shugaba Tinubu ya kaddamar da jiragen ruwa guda uku sannan ya yaba da yadda Sojin Ruwan ke yaki da ‘yan fashi a teku, da satar man fetur, da kamun kifi ba bisa ka’ida ba, da sauran laifuka a yankin Gulf of Guinea.
Ya ce hakan ya inganta tsaro tare da kara samar da man fetur.
Shugaba Tinubu ya kuma gode wa kasashen waje da suka halarci bikin, yana mai cewa hakan ya nuna hadin gwiwa wajen kare teku.
Ya ce ruwan Najeriya na da arziki kuma ginshikin tattalin arzikin kasar ne.
Daga karshe ya yi alƙawarin ci gaba da baiwa Rundunar Sojin Ruwan kayan aiki, da fasaha da horo, sannan ya taya babban hafsan Sojin Ruwa, Vice Admiral Idi Abbas, da jami’ai da iyalansu murna.
Da nasa jawabin, Vice Admiral Abbas ya ce nasarorin da suka samu sun samu ne saboda goyon bayan gwamnati, da sayen Sababbin jiragen ruwa, da hadin gwiwa da sauran hukumomi.
Ya yi alƙawarin ci gaba da amfani da fasaha wajen kare ruwan Najeriya.
Manyan baki a wajen taron sun hada da Gwamnan Legas Babajide Sanwo-Olu, da Gwamnan Kwara AbdulRahman AbdulRazaq, da Mai baiwa Shugaba shawara akan tsaro Nuhu Ribadu, da da manyan jami’an tsaro.
