
Ministan ƙasa a ma’aikatar tsaron Nijeriya, Bello Matawalle, ya bayyana kwarin gwiwa kan cewa masu kaɗa ƙuri’a a Arewacin Nijeriya za su mara wa Shugaba Bola Tinubu baya a zaɓen 2027 domin nuna godiya ga ayyukan ci gaba da gwamnatinsa ke aiwatarwa a yankin.
Matawalle ya ce Arewa ta amfana matuƙa daga manyan ayyukan gine-ginen ababen more rayuwa da sauran shirye-shiryen ci gaba da gwamnatin Tinubu ta ƙaddamar tun bayan hawanta mulki.
Ya kuma ce an naɗa mutane da dama daga yankin Arewa a muhimman mukaman gwamnati, inda suke taka rawa wajen tabbatar da cewa al’ummomin yankin sun ci moriyar dimokuraɗiyya.
Ministan ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi ga magoya baya da shugabannin jam’iyya da suka kai masa ziyarar gaisuwar Sallah a gidajensa da ke ƙananan hukumomin Maradun da Gusau na jihar Zamfara.
A cewar sa, al’ummar yankin Arewa baki ɗaya ba su da wani ɗan takarar shugaban ƙasa mafi dacewa a zaɓen 2027 fiye da Tinubu, kamar yadda Daily Nigerian ta ruwaito.
Ya bayyana ayyukan gine-ginen tituna da ake yi kamar faɗaɗa titin Abuja–Kaduna–Zaria–Sakkwato da kuma titin Badagry–Ilela a matsayin hujjar yadda gwamnatin ke ƙoƙarin bunƙasa yankin.
Matawalle ya yi kira ga al’ummar Arewa da kada su bari wasu ‘yan siyasa da ya bayyana a matsayin masu son zuciya kuma marasa kishin ci-gaban ƙasa su rinjaye su.
