
Sama da mahajjata miliyan 1.6 ne suka hallara a yau a filin Arafat domin gudanar da ɗaya daga cikin manyan ginshikan ibadar aikin Hajji.
Mahajjatan daga sassa daban-daban na duniya sun fara kwararowa tun daga safiyar yau zuwa filin na Arafat, inda ake sa ran za su kwashe tsawon yini suna gudanar da addu’o’i, neman gafara da kuma ambaton Allah cikin yanayi na tawali’u da natsuwa.
Malaman addinin Musulunci sun bayyana ranar Arafat a matsayin ɗaya daga cikin ranaku mafiya falala a addinin Musulunci, wacce take cike da rahama da gafarar zunubai ga bayin Allah.
Mahajjatan na gudanar da Talbiya tare da roƙon Allah Ya karɓi ibadunsu, yayin da wasu ke karanta Alƙur’ani da yin zikiri a wurare daban-daban na filin Arafat.
Hukumomin Saudiyya sun ce sun samar da tsare-tsare na musamman domin tabbatar da sauƙin zirga-zirga, kula da cunkoson jama’a da kuma samar da ingantattun ayyukan lafiya da agajin gaggawa domin kare lafiyar alhazai.
Haka kuma hukumomin lafiya sun shiga shirin ko-ta-kwana saboda tsananin zafin rana da ake hasashen zai haura maki 45 a ma’aunin yanayi.
An buƙaci mahajjata da su riƙa yawaita shan ruwa, amfani da laima da kuma kaucewa yawan tsayuwa a ƙarƙashin rana domin guje wa matsalolin da zafi ka iya haifarwa.
