Ku dawo da motocin da ku ka tafi da su – AKY gaTsoffin Kwamishinonin da su ka bi Kwankwaso
By: Mutawakkilu
Cibiyar yaɗa labarai ta gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf (AKY Media Centre) ta bukaci tsoffin Kwamishinonin da suka ajiye mukamansu a kwanaki baya da su dawo da duk kadarorin gwamnati dake hannunsu kamar yadda doka ta tanada.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Cibiyar da rabawa manema labarai a kano.
Idan za a iya tunawa waɗannan tsofaffin kwamishinonin sun sauka daga mukamansu ne da kansu, saboda ba za su goyi bayan matakin gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya dauka na komawa jam’iyyar APC ba. Haka kuma suka bayyana biyayyarsu ga jam’iyyar NNPP da ke goyon bayan Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.
Cibiyar ta zargi cewa tun bayan saukarsu daga mukaman, wasu daga cikinsu sun ƙi mayar da motocin gwamnati da aka ba su domin aikin ofis. Ta ce motocin ba kyauta ba ne, mallakin gwamnati ne, kuma an ba su ne domin gudanar da ayyukan gwamnati kaɗai.
A cewar sanarwar, dokoki da ƙa’idojin aikin gwamnati sun tanadi cewa duk wanda ya sauka daga mukami ko ya kammala wa’adinsa, wajibi ne ya miƙa duk wata kadara ta gwamnati da ke hannunsa. Ta ƙara da cewa hakan ba zaɓi ba ne, dole ne a bi shi doka.
Cibiyar ta bayyana damuwa kan rahotannin da ke cewa wasu daga cikin tsoffin jami’an sun riƙe fiye da mota guda ɗaya, ciki har da motocin Hilux da aka tanada domin ayyukan ofis. Duk da wasiku da umarnin hukuma da aka aike musu na su mayar da motocin nan take, an ce sun yi biris da hakan.
Sanarwar ta ce wannan mataki ya na nuna kamar tsofaffin kwamishinonin sun rike motocin ba sa son mayarwa gwamnatin Jihar Kano, lamarin da ke bayyana a matsayin keta doka, cin amana da rashin girmama alhakin da ke tattare da riƙon muƙamin gwamnati.
Ta kuma jaddada cewa Gwamnatin Jihar Kano ba za ta zuba ido a riƙe kadarorin jama’a ba bisa ƙa’ida ba, inda ta yi alƙawarin ɗaukar duk matakan doka da na gudanarwa domin kwato motocin tare da tabbatar da an hukunta masu laifi.