
Daga Mohammed Babagana Abubakar
A dandalin siyasar Nijeriya, akwai wasu ‘yanwasa da suka kware wajen abin da masu nazari ke kira dabarar kawar da hankali: wato haifar da hayaniya mai yawa kan zargin rashin adalci a daidai lokacin da tasirinsu a siyasa ke dusashewa. Kalaman da Alhaji Buba Galadima ya rika yi a baya-bayannan kan Mai Girma Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf, da kuma Daraktan Hukumar Tsaro ta DSS a Kano, misali ne karara na wannan salo. Zarge-zargen rashin adalci da kuma kama masu adawa da gwamnati da cewar ana farautarsu na nuna tamkar jihar na cikin rikici. Amma idan aka yi duba na gaskiya da idon basira, labarin ya sha bamban matuƙa.
Ba abin mamaki ba ne cewa hare-haren Galadima sun ƙaru nan take bayan cire shi daga kujerar Shugaban Majalisar Gudanarwa ta Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano (Kano State Polytechnic) a watan Fabrairu 2026. Gwamna Yusuf, bisa manufarsa ta Kano First Agenda, wani tsarin gudanar da mulki da ke mayar da hankali kan inganta cibiyoyi da fifita ci gaban Kano, ya sauke Galadima daga mukamin, yana mai nuni da bukatar inganta aiki da sake farfaɗo da cibiyar. Daga bisani, aka naɗa Sarkin Gaya, Alhaji Aliyu Abdulkadir, wanda darajarsa da kusancinsa da al’umma suka dace da burin sake fasalin da Gwamnan ke nema.
Ga mutumin da ya riƙe babban mukami a wata jiha da ba jiharsa ba, abin da ya fi dacewa shi ne barin mukamin cikin mutunci da kima. Amma maimakon haka, Galadima ya zaɓi ramuwar gayya. Kamfen dinsa na kafafen yaɗa labarai, wanda ke ƙaruwa a kowace hira, ba dabi’ar mai fafutukar dimokuraɗiyya ba ce. Dabi’a ce ta wanda aka cire masa damar cin moriyar mukami, kuma yake son ya sa a biya farashin siyasa kan hakan.
Zarge-zargen da Galadima ya yi, ciki har da batun kama wani mai shirin rediyo da kuma bayyana matakan jami’an tsaro a matsayin tsangwama ta siyasa, ƙoƙari ne na karkatar da gaskiyar tsarin mulki da aikace-aikacen gwamnati a Kano. A halin yanzu, Kano na tafiya a cikin yanayi mai sarkakiya ta fuskar tsaro da siyasa, musamman ma bayan da Gwamnan ya yi sauyin sheka ta siyasa zuwa APC, wanda ya buƙaci daidaita siyasar jihar cikin sabon yanayin ikon ƙasa. A irin wannan yanayi, ayyukan DSS suna gudana ne bisa dokar tarayya, hurumin hukuma, da kuma sahihan korafe-korafe, ba bisa umarnin siyasa ba.
‘Yancin faɗin albarkacin baki, wanda Sashe na 39 na Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Nijeriya ya tanada, hakki ne da gwamnatin Gwamna Yusuf ta mutunta. Amma babu wani sashe na kundin da ke bai wa mutum damar amfani da kafafen yaɗa labarai don tunzura rikici, yada ƙarya da aka tabbatar, ko aikata laifukan da Dokar Yaki da Laifukan Yanar Gizo (Cybercrime Act 2015) ta haramta. Idan jami’an tsaro suka gayyaci wani domin amsa tambayoyi bisa sahihancin korafe-korafe a ƙarƙashin wannan doka, wannan aiki ne na bin doka da oda. Kiransa da “garkuwa ta siyasa” ba fafutukar dimokuraɗiyya ba ce; misali ne na ɓata suna da gangan.
Yayin da Galadima ke gina labarin tsangwama, gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf na gina abin da ya fi muhimmanci, rikodin mulki. Gwamnatin ta fara gyaran manyan makarantun gaba da sakandare na jihar, tana magance matsalolin da suka daɗe suna faruwa. Ta ɗauki matakan biyan basussukan garatuti ga ma’aikatan gwamnati da suka yi ritaya, alƙawarin da gwamnatocin baya suka kasa cikawa. Haka kuma, ta fara rushe tsarin siyasar ubangida, inda aka daɗe ana mayar da cibiyoyin gwamnati tamkar mallakin masu iko maimakon al’umma.
Wannan rushewar tsarin siyasar gata ne da ke bayyana ainihin dalilin da ke bayan kamfen ɗin Galadima. Ba wai ya ƙi tsarin mulkin Gwamna Yusuf ba ne; abin da yake ƙi shi ne sabon yanayin da ba ya ba da tabbacin samun mukamai da tasiri bisa alaƙar siyasa kaɗai. Cire shi daga kwalejin ba kawai sauyin aiki ba ne; alama ce cewa tsoffin tsare-tsare sun ƙare. Martaninsa kuwa shi ne ƙoƙarin nuna cewa irin waɗannan matakai suna da tsada a siyasa. Amma Gwamna Yusuf da gwamnatinsa dole ne su ci gaba da tafiya ba tare da gezau ba.
Al’ummar Kano ba kawai kallo suke ba, kuma ba za a yaudare su ba. Suna da wayewar siyasa da tarihin fahimta mai zurfi, kuma suna iya bambance tsakanin fafutukar dimokuraɗiyya ta gaskiya da siyasar ƙorafi wadanda suka rasa madogara. Galadima ba ya yaƙi ne don talakawan Kano; yana yaƙi ne don mukami da aka raba shi da shi, gata da aka janye, da tasirin siyasa da ya rasa. Wannan haƙƙinsa ne. Amma ya kamata a kira shi da sunansa na gaskiya.
An zaɓi Gwamna Abba Kabir Yusuf ne domin ya yi mulki bisa muradun al’ummar Kano, ba don kiyaye damar gata ta wasu ba. Gwamnatinsa, DSS, da dukkan cibiyoyin da ke aiki bisa hurumin kundin mulki dole ne su ci gaba da mai da hankali kan wannan manufa, ba tare da shagaltuwa da hayaniyar masu jin zafin rasa gata ba. Makomar Kano za ta ginu ne da nagartaccen mulki, aiki tukuru, da rikon amana, ba kan ƙorafe-ƙorafen da aka ƙirƙira domin dawo da tsohuwar daula ba.
GAME DA MARUBUCIN
Mohammed Babagana Abubakar mai sharhi ne kan siyasa da nazarin al’amuran mulki, mai sha’awar batutuwan rikon amana, ingantaccen shugabanci, da ci gaban dimokuraɗiyya a Kano da Arewacin Nijeriya.