Mutawakkilu Ibrahim 
Gwamnatin jihar Kano ta kaddamar da wani kwamiti mai karfi na wayar da kan jama’a ‘yan kasa da su shigo suyi rijistar katin zabe
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta fara yin rijistar masu kada kuri’a a fadin kasar nan, Jihar Kano tayi wani gagarumin shiri na yin rijistar masu kada kuri’a miliyan 10. A martanin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya mayar, ya kaddamar da kwamitin da ke kula da rajistar masu kada kuri’a domin gudanar da yakin neman zabe a fadin jihar.
Da yake jawabi a wajen bikin Kaddamar da kwamitin Gwamnan kano wanda Sakataren Gwamnatin Jihar, Alhaji Umar Farouk Ibrahim ya wakilta ya jaddada muhimmancin wayar da kan ‘yan kasa domin su taka rawar gani wajen gudanar da ayyukan. “Rijistan masu kada kuri’a ya wuce aikin jama’a, nauyi ne na tilas,” in ji Ibrahim, inda ya kara da cewa shirin na da matukar muhimmanci wajen tsara makomar Kano da Najeriya baki daya.
A cewar faruk, kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, kwamishinan yada labarai da al’amuran cikin gida ne zai jagoranci kwamitin, tare da tallafawar mambobi 36 da suka fito daga sassa daban-daban.
Wadannan sun hada da wakilai daga ofishin mataimakin gwamna, masu ba gwamna shawara na musamman, da kwamishinan harkokin mata, da mai ba da shawara na musamman kan yada labarai.
Kwamitin ya kuma hada da dimbin masu ruwa da tsaki kamar wakilin Mai Martaba Danmalikin Kano, Alhaji Auwalu Mudi Yakasai, Malaman addini (Ulama), ’yan kasuwa, mambobin kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya (NUJ), da kuma kungiyar matasa ta jiha. “Wannan kwamiti ne na kowa, har ma jam’iyyun adawa suna da wakilci,”
Da yake karin haske kan aikin, Ibrahim ya nuna cewa a halin yanzu Kano na da masu rajistar zabe kimanin miliyan biyar. “Muna sa ran rubanya wannan adadi zuwa miliyan goma. Wannan ba adadi ba ne kawai, yana nuni da kudurinmu na shiga dimokradiyya,” in ji shi. Ya bukaci rundunar da ta tabbatar da yin adalci, gaskiya da kuma hada kai a duk lokacin da ake yin rajistar.
Wakilin Gwamnan ya kuma bukaci kwamitin da ya hada kai da INEC don tabbatar da cewa an samar da isassun kayan aiki nayin rajista. “Kada ku takaita kanku ga abubuwan yau da kullun. Ku fara yakin neman wayar da kan jama’a a dukkan kananan hukumomi 44,” in ji shi.
Ibrahim ya kuma jaddada bukatar ganin an magance rashin jin dadin masu kada kuri’a da kuma tabbatar da cewa sabbin runfunan zabe da aka kirkiro sun samu kulawar da ta dace. Ya kara da cewa “Tsarin tattara bayanai yana da matukar muhimmanci, yin rijista abu daya ne, amma tabbatar da cewa masu rajistar sun tattara katunan zaben su wani muhimmin mataki ne,” in ji shi.
A nasa jawabin, shugaban kwamitin kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ya nuna jin dadinsa da samun damar yin hidima. “Muna daukar wannan aikin a matsayin kira zuwa ga al’uma, muna tabbatar wa mai girma gwamna cikakken alkawarinmu kuma, Insha Allahu, ba za mu ba shi kunya ba,” in ji Waiya.
Ya yi nuni da cewa, kwamitin ya kunshi mutane masu tasiri da kuma kananan hukumomi inda aka sanya su don su zaburar da ‘yan kasa yadda ya kamata. Waiya ta ce “Muna kira tun daga kan shugabanni na kasa har zuwa kan wakilan sarakuna da sushigo don samun nasarar wannan yakin.”
A yayin da ake ci gaba da gudanar da aikin rijistar masu kada kuri’a, jajircewar da jihar Kano ta yi na samar da masu kada kuri’a miliyan 10 na nuni da cewa, an sake yin alkawarin tabbatar da dimokuradiyya da kuma daukar nauyin al’umma.
Za mu tabbatar da cewa mutane sun yi rajista sun yi amfani da PVC ɗin su tunda Kano ce kan gaba a siyasar Najeriya.
