By Khadijah Shehu Abdulkareem 
Gwamnatin ta bayyana cewa tun a watan Janairun 2024 gwamna Abba Kabir Yusuf ya kafa Majalisar Dattawan jihar ta Kano, wato (KEAC) wadda za ta riƙa ba da shawara kan ci gaban al’umma.
Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labarai da harkokin cikin gida, Ibrahim Abdullahi Waiya ya fitar a yau Laraba.
Sanarwar ta ce “Tun bayan sanar da kafa wannan majalisar, ana ci gaba da shirye-shiryen da suka dace domin tabbatar da ingantaccen tsarin da zai ba da damar fara aiki yadda ya kamata.”
Sanarwar ta ƙara da cewa “Wannan majalisar ba ta da wata alaƙa da siyasa ko jam’iyya, sai dai ta kasance dandalin bayar da shawara bisa hikima da gogewa.”
